DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar ya nuna damuwarsa kan sace dalibai a jihar Kebbi

-

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan harin da aka kai Makarantar ‘yan mata ta Gwamnati da ke Maga a Jihar Kebbi, wanda ya yi sanadin mutuwar mataimakin shugaban makarantar da kuma sace wasu dalibai inda ya wannan al’amari ya sake tabbatar da irin tabarbarewar tsaron da ƙasar ke fuskanta.

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na facebook, Atiku ya kuma yi Allah-wadai da kisan jigon APC, Umar Moriki, da kuma sace iyalai da dama a karamar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, yana mai bayyana wadannan hare-haren a matsayin aikata barna da ya sabawa duk wata al’umma mai bin doka.

Google search engine

Hakazalika, ya kuma ambaci irin tashin hankalin da ake fama da shi a Jihar Filato, Benue da wasu yankuna, inda ya ce al’ummomi na ci-gaba da fuskantar hare-hare.

Haka ma a karama Hukumar Shanono ta Kano, ya jaddada cewa mutanen yankin na tserewa daga gidajensu saboda fargabar hare-hare.

Madugun adawar ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta sake fasalin tsaro, ta ƙara yawan jami’an tsaro a yankunan da abin ya fi shafa tare da ƙara amfani da bayanan leƙen asiri wajen dakile hare-hare sannan kuma ya ce ’yan Najeriya sun cancanci kariya, mtuntawa da zaman lafiya.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara