DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore ya yi Allah-wadai da sace dalibai a jihar Kebbi

-

Dan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya yi Allah-wadai da sace ‘yan mata 25 daga Makarantar sakandare ta gwamnati, da ke a Maga, a karamar hukumar Danko-Wasagu ta jihar Kebbi, tare da kiran addu’a ga wadanda abin ya shafa.

Moore ya ce duk da har yanzu ba su samu cikakken bayani ba kan wannan mummunan hari, amma ya bayyana cewa yana kyautata zaton ya faru ne a wani yanki na Kiristoci a Arewacin Nijeriya, kuma ya bukaci hukumomi su dauki kwakkwaran mataki.

Google search engine

An kai harin ne da safiyar ranar Litinin, inda ‘yan bindiga suka shiga makarantar da makamai, suka hallaka mataimakin shugaban makarantar, tare da raunata wasu ma’aikata, sannan suka sace ‘yan mata 25 kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban hafsan sojin kasa ya umurci sojoji da su tsaurara wajen ganin sun ceto dalibai mata da aka sace a jihar Kebbi

Babban hafsan rundunar sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun Operation Fansan Yamma da su matsa kaimi wajen ceto daliban GGCSS Maga da...

’Yan bindiga sun sace fasinjoji shida a hanyar Ogobia–Adoka a Benue

’Yan bindiga sun tare wata motar haya suka tafi da fasinjoji shida sannan suka kashe direba a hanyar Ogobia–Adoka da ke ƙaramar hukumar Otukpo a...

Mafi Shahara