DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Sokoto ta kammala aikin samar da lantarki na kashin kanta na N7bn

-

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kammala aikin gina tashar samar da wutar lantarki ta mai zaman kanta, kamar yadda Kwamishinan Makamashi, Alhaji Sanusi Danfulani, ya bayyana yayin ziyarar duba aikin da aka kai ranar Laraba.

Kamar yadda Kwamishinan ya shaida wa manema labarai, gwamnatin jihar ta zuba biliyoyin naira a aikin, tare da ƙarin N1.5bn da Gwamna Ahmad Aliyu ya saki kwanan nan domin gyare-gyare da kammala aikin.

Google search engine

A yayin da yake karin haske, Daraktan Sashen Lantarki na ma’aikatar, Injiniya Abubakar Shehu, ya bayyana cewa an gwada wasu sassan injinan a makon da ya gabata, sai dai ya ƙi fayyace matakin da gwamnati za ta ɗauka kan yadda za a tura wutar zuwa jama’a, yana mai cewa wannan ya rage ga hukumomin wutar lantarki.

Rahotanni sun nuna cewa aikin na megawatt 38 an bai wa kamfanin Vulcan Capital Energy na Amurka ne a 2008 kan kuɗin N3.8bn da wa’adin watanni shida, amma an yi ta tsawaita lokacin kammalawa daga 2009 zuwa 2010, 2011, 2013, 2014, 2016 har zuwa 2019 kafin a ce yanzu an kammala shi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Amnesty International ta koka kan halin da jihar Katsina ke ciki kan batun tsaro

Kungiyar kare hakin bil’adama ta Amnesty International ta gargadi cewa hare-haren ’yan bindiga da ƙungiyoyin ta’addanci suna tura Jihar Katsina zuwa ga mummunan bala’in jin-kai,...

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai a jihar Kebbi da DCL Hausa ta yi rahoton zargin da ake yi masa...

Mafi Shahara