DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amnesty International ta koka kan halin da jihar Katsina ke ciki kan batun tsaro

-

Kungiyar kare hakin bil’adama ta Amnesty International ta gargadi cewa hare-haren ’yan bindiga da ƙungiyoyin ta’addanci suna tura Jihar Katsina zuwa ga mummunan bala’in jin-kai, yayin da dubban al’ummomi ke tserewa daga gidajensu saboda tsananin rashin tsaro.

A cewar kungiyar, mutane da dama sun rasa matsuguni, yara na mutuwa saboda ƙarancin abinci, sannan iyaye, musamman mata, na kallo rayukan yarensu na salwanta a gaban idanuwansu. Amnesty International ta rawaito cewa Kungiyar likitoci ta MSF ta tabbatar da cewa yara 652 sun mutu sakamakon matsanancin rashin abinci cikin watanni shida na farko na bana.

Google search engine

DCL Hausa ta ruwaito cewa Amnesty International ta nuna damuwa matuƙa kan yadda mutane a ƙananan hukumomi 13 cikin 34 ke fama da hare-hare, garkuwa, kwace amfanin gona da ƙona gidaje, lamarin da ya hana ma’aikatan jin-kai shiga da agajin gaggawa.

Kididdigar UNICEF ta nuna cewa yara sama da 300,000 ba sa zuwa makaranta a Katsina saboda tsaro, tare da karin dubban yara a Dandume, Jibiya, Safana, Batsari, Faskari, Funtua da Kankia da ke fama da matsananciyar rashin lafiya da abinci. Amnesty International ta bukaci gwamnatin tarayya da ta jihar Katsina su dauki mataki na gaggawa wajen kawo ƙarshen wannan tashin hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara