Majalisar dinkin duniya ta yi kakkausar suka kan sace ɗalibai da malamai daga makarantar St. Mary’s a Papiri, jihar Neja, inda ta ce harin abin takaici ne kuma makarantu wajibi ne su kasance wuraren kariya ga ɗalibai.
A cewar kungiyar Kiristocin Nijeriya, CAN, ’yan bindigar sun sace ɗalibai 215 da malamai 12, lamarin da ya zo kwanaki bayan sace ɗalibai 25 da kashe malami a Maga, da ke jihar Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
MDD ta ce dole a mai da hankali kan ganin an dawo da yaran cikin gaggawa, ta kuma jaddada bukatar aiwatar da yarjejeniyar kariyar makarantu, yayin da gwamnatin Nijeriya ta rufe makarantun Unity 41 domin guje wa sake faruwar irin wadannan hare-haren.



