Gwamnatin Amurka ta ce gwamnatin shugaba Donald Trump na aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin kawo ƙarshen abin da ta kira zaluntar Kiristoci da ’yan tada kayar baya ke yi a kasar, kamar yadda sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana.
Hegseth ya bayyana haka ne a shafinsa na X da Facebook bayan ganawarsa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da tawagarsa a Amurka.
A cewar sakataren, sun tattauna kan tashin hankaulan da ke addabar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce gwamnatin Trump na kokari sosai don dakile hare-haren da ake danganta wa ’da ‘yan tada kayar baya.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ribadu ya jagoranci tawaga mai ƙarfi zuwa Amurka domin tattaunawa kan zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda kuma kafin haka shugaba Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake kallon suna da matsalar tauye ’yancin addini.



