DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Trump na Amurka ya sake aibata Nijeriya inda ya zargi gwamnati da gazawa a harkar tsaro

-

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake sukar Nijeriya, inda ya kira ta da “abin kunya” tare da zargin gwamnati da kasa dakile kashe-kashen da ake yi wa ’yan ƙasa. Ya ce ana kashe mutane dubbai ba tare da wani mataki ba, inda ya zargi gwamnati da gazawa.

Kalaman Trump sun zo ne bayan ya sake saka Nijeriya a jerin ƙasashen da ake kula da su na musamman, yayin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta tura mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, zuwa Amurka don gabatar da bayanai kan matakan tsaro.

Google search engine

Tun bayan kalaman Trump, hare-haren sun ƙaru a yankuna daban-daban inda ‘yan bindiga suka halaka babban hafsan soja a Borno, yayin da barayin daji suka sace dalibai mata 25 a Kebbi tare da halaka mataimakin shugaban makarantar.

A ciki ƙarin hare-haren, ’yan bindiga sun kutsa coci a Eruku, Kwara, sannan suka sace fiye da ɗalibai 300 da malamai 12 daga makarantar St Mary’s a Papiri, Jihar Neja, abin da ya kara nuna tsananin tabarbarewar tsaro a ƙasar kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara