DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Firaministar Italiya ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta kare rayukan Kiristoci a kasar

-

Fira-ministar kasar Italiya, Giorgia Meloni, ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta kara tsaurara matakan tsaro domin kare Kiristoci a sassa daban-daban na Nijeriya.

A wata sanarwa da ta wallafa a X a ranar Juma’a, Meloni ta bayyana harin da aka kai wa al’ummomin Kirista a Nijeriya a matsayin mummuna kuma abin ƙyama. Ta bukaci hukumomi su dauki matakin gaggawa domin hukunta masu aikata irin wadannan laifuka.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Meloni ta ce ’yancin yin addini hakki ne da ba ya karyewa, tana mai jaddada cewa dole ne gwamnati ta kare dukkan rukunan addinai ba tare da wariya ba.

Haka kuma ta nuna alhini ga iyalan da lamarin ya shafa da al’ummomin da ke fargaba sakamakon hare-haren da ake kai musu.

Wannan furuci ya fito ne a lokacin da ake cikin damuwa kan yadda hare-haren ’yan bindiga, ’yan ta’adda ke kamari kan al’umma a Nijeriya, tare da sace-sace da kai farmaki ga kauyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara