Rahotanni sun yi nuni da cewa an sake yunkurin yin juyin mulki a kasar Guinea-Bissau.
Wannan ya zo ne bayan da shugaba mai ci Umaro Sissoco Embaló ya bayyana hasashen sa na samun nasara a zaben shugaban kasar da ya gudana a makon da ya gabata da kashi 65 na kuri’u.
’Yan jarida da ke ruwaito zabe sun bayyana cewa lamarin tsaro ya taɓarɓare a babban birni, inda aka jiyo karar harbe-harbe a kewayen ofishin hukumar zabe ta kasar (CNE).



