Kasashen Nijar da Chadi sun kammala wani taron hadin gwiwa na kwanaki biyu da suka gudanar a birnin N’djamena na kasar Chadi karkashin jagorancin Firaministocin kasashen biyu.
A yayin taron kasashen biyu sun kara jaddada dadaddariyar yarjejeniyar dangantakar da ke a tsakaninsu tare da rattaba hannu kan wadansu sabbi.
Nijar da Chadi na da dadaddiyar dangantaka mai kyau a tarihi a matsayin su na kasashe makwabtanta juna.



