DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata amarya ta yanke mazakutar angonta a Katsina

-

Wata mata mai suna Nana da ke da kimanin shekaru 17 ta sa reza ta yanke mazakutar mijinta a daren farko da ya tare bayan ya aure ta a kauyen ‘Yar Kyasuwa na karamar hukumar Kafur ta jihar Katsina.
Majiyar DCL Hausa a kauyen ta ce mijin mai suna Malam Abubakar ya hadu da matar a lokuttan baya, da yake zuwa zawarci, har ya yi nasarar aurenta. Bayan an daura aure ne, ya tare a daren Lahadi wayewar Litinin, ake zargin ta sa reza ta yanke masa mazakuta.
Har ya zuwa lokacin hada wannan labari, ba a kai ga sanin dalilin wannan mata na yanke wa mijinta wannan hukunci ba. Amma dai, mijin na asibitin Kwandala na garin Malumfashi yana karbar magani.
Sai dai bayanan da DCL Hausa ta tattara sun ce yanzu haka matar ta shiga hannun jami’an tsaron ‘yan sanda. Duk da rahotanni sun ce mutumin na jin jiki, bayan wannan aika-aika da ake zargin wannan sabuwar mata ta aikata masa.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta hannun kakakinta ASP Aliyu Abubakar, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce yanzu haka ana cigaba da gudana da bincike, da zarar an kammala, za a maka matar kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara