DCL Hausa Radio
Kaitsaye

AU ta kori jamhuriyar Nijar daga cikin ta

-

Kungiyar tarayyar Africa ta sanar da korar
jamhuriyar Nijar daga cikin ta, abinda ke zama wani hukunci na baya-bayan nan
da aka yankewa Nijar bayan juyin Mulkin watan jiya.

Bayan taron kungiyar na yau Talata a
birnin Addis Ababa, kungiyar ta ce daukar wannan mataki ya zama wajibi la’akari
da yadda sojojin na Nijar suka ki bada hadin kan da ya dace a game da
tattaunawar Diplomasiyya.

Matakin na AU na zuwa ne bayan da tuni
ECOWAS da wasu kungiyoyin kasashen ketare suka sanar da kakabawa Nijar din
takunkumai, wadanda tuni suka fara tasiri a kanta.

Sai dai kuma masana na ganin
cire Nijar daga cikin AU ba zai yi mata wani tasiri ba, la’akari da yadda kungiyar
ke zama tamkar dai ‘yar amshin shatan kasashen yamma a wasu lokutan.

Bayan wannan
mataki, kungiyar ta AU ta kuma ce zata bibiyi irin matakan da kungiyar ECOWAS
ko CDEAO ta dauka kan jamhuriyar Nijar, don ganin ta inda ya kamata ta kara
shiga da nufin kara matsa lamba ga sojojin na Nijar.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada mahajjaci ya rike kudin da suka wuce Riyal 60,000 a kasar Saudiyya – Jan hankalin NAHCON ga Alhazan Nijeriya

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta shawarci mahajjatan kasar da su guji daukar kudi sama da Riyal 60,000 na Saudiyya domin...

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

Mafi Shahara