DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Son Nijeriya ne ya sa muke son dawo da Bazoum a Nijar – Tinubu

-

https://drive.google.com/uc?export=view&id=11NV5sySC5phE0Zv-H9-LqJQE7ZbFOO6p
Shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS Bola Tinubu ya ce shi da kansa ya gamsu yaki da kasar Nijar ka iya haifar da matsaloli ga yunkurinsa na samar kofofin arziki ga ‘Yan Nijeriya. Amma a cewarsa, kokarin da ECOWAS ke yi na dawo da Nijar cikin hayyacinta, yunkuri ne na kare muradu da martabar Nijeriya.
Tinubu ya fadi haka ne a yayin wata ganawa da ya yi a ranar Jumma’a da jakadan Amurka a Nijeriya. Shugaban na ECOWAS ya ce yana da matukar muhimmanci ECOWAS ta yi amfani da hanyoyin da suka wajaba wajen dawo da dimukuradiyya da hana sojojin tsawaita zamansu a Nijar .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Mafi Shahara