DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An fara caccakar Tinubu bisa yadda yake rabon mukamai

-

Kungiyar marubutan da ke kare hakkin bil’adama ta HURIWA ta zargi shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu da nada mukamai a tsakanin ‘yan’uwa da aminnan arzikinsa kadai, inda kungiyar ta yi zargin cewa yana nada muhimman mukaman ne daga ‘yan kabilar Yarabawa.
Kungiyar ta yi wannan zargin ne a cikin wata sanarwa daga babban jami’inta Emmanuel Onwubiko, inda sanarwar ta yi magana kan nadin Gwamnan babban bankin kasa CBN da shugaban hukumar tattara kudin haraji ta FIRS da Shugaba Tinubu ya yi a kwana-kwanan nan, da ya nada duk Yarabawa.
Kungiyar ta bukaci shugaba Tinubu da kada irin layin da tsohon shugaban kasa Buhari ya bi wajen irin wadannan mukamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara