DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci Tinubu da ya karya farashin kayan masarufi

-

 Kotu ta umurci Tinubu da ya karya farashin kayan masarufi

Google search engine

Babbar Kotun tarayya da ke zamanta a Jihar Legas, ta umarci Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ta daidaita farashin kayayyaki da na man fetur, a cikin kwanaki bakwai.

Alƙalin Kotun Mai shari’a Ambrose Lewis-Allagoa, shine ya bada umarnin a yayin zaman kotun, bayan da Lauyan nan mai fafutuka, Mista Femi Falana (SAN) yayi Ƙarar Gwamnatin kan hauhawar farashin kayayyaki a kasar.

Falana ya shigar da ƙarar ne, inda ya dogara da sashe na 4 na dokar kayyade farashin kayayyaki, kuma tuni kotun ta umarci gwamnati da ta gyara farashin kayayyakin.

Kayan da umarnin ya shafa sun haɗar da madara, gari, gishiri, sukari, kekuna, ashana, babura, motoci, man fetur, gas da kuma kalanzir.

Kuma dai Alkalin kotun ya bayar da umarnin ne ga Ministan shari’a na Nijeriya da kuma Hukumar Kula da Farashi Kaya ta ƙasar (PCB).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Mafi Shahara