DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun hallaka Kwamandan jami’an sa kai na ‘Community Watch Corp’ a jihar Katsina

-

Sanusi Hassan Gambo, wanda tsohon jami’in dan sanda ne da ya yi ritaya, DCL Hausa ta samu labarin cewa dama ya takura wa ‘yan ta’addar da ke aiki a wannan yanki na karamar hukumar Kankara.
Majiyar DCL Hausa ta tabbatar da cewa Kwamandan ya fita aiki ne tare da jami’an ‘yan sanda na ‘mopol’ a lokacin da ya cimma lokacinsa. Sai dai had yanzu babu takamaiman halin da su ‘yan sandan da suka fita aiki tare suke ciki ya zuwa lokacin hada wannan labari.
Lamarin dai ya faru ne da safiyar Larabar nan a cikin dajin Kankara a lokacin da rahotanni suka nuna cewa sun je kakkabe wasu ‘yan ta’adda ne.
A watan Oktobar, 2023 ne Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya kaddamar da jami’an sa kan na Community Watch Corp’ su 2,400 domin tallafar jami’an tsaron gwamnati a yaki ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara