DCL Hausa Radio
Kaitsaye

UAE ta ɗage haramcin visa kan yan Najeriya

-

Hadaddiyar Daular Larabawa ta ce za ta dawo da bayar da biza ga ‘yan Najeriya, hakan wani mataki ne na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.

Google search engine

Bayanin hakan na a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Talata.

Wannan dai na zuwa ne shekaru biyu bayan da Daular Larabawa ta sanya wa yan Najeriya takunkumin shiga kasar.

A cewar hukumomin Hadaddiyar Daular Larabawar an dawo da shirin ya fara aiki ne daga ranar 4 ga watan Maris din shekarar 2024, wanda hakan ya samo asali ne sakamakon tattaunawa tsakanin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na UAE, Sheikh Mohamed bin Zayad Al Nahyan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara