DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An saka lokacin sake kidayar yawan al’ummar Nijeriya

-

An saka lokacin sake kidayar yawan al’ummar Nijeriya

Hukumar kidaya ta kasa (NPC) ta ce zatayi kidayar ‘yan kasar a watan Nuwamba, 2024, don kidayar yawan al’umma da gidaje a Nijeriya.

Google search engine

Da yake jawabi yayin wani taron manema labarai na bikin ranar yawan jama’a ta duniya na shekarar 2024, shugaban hukumar, Nasir Isa Kwarra, ya ce shawarar hakan ta kasance bisa amincewar shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kwarra, wanda ya bayyana cewa hukumar ta shirya kashi 70 cikin 100 na gudanar da kidayar, ya ce jinkirin da Nijeriya ke samu na samun bayanan al’ummarta ba zai hana kasar samun nasarar kidayar yawan jama’a da gidajen dake kasar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara