DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Firgici ya kunno kai a Rano da ke Kano bayan da wasu masu kama da ‘yan daba suka mamaye fadar masarauta

-

Firgici ya kunno kai a Rano da ke Kano bayan da wasu masu kama da ‘yan daba suka mamaye fadar masarauta

A cikin wata wasika da aka rubuta wa kwamishinan ‘yan sandan jihar, jaridar SolaceBase ta rawaito cewa ‘yan dabar sun yi sansani a fadar Sarkin Rano tun a ranar Lahadi da wasu da ba a tantance ko suwaye ba.

Google search engine

Ta ce har yanzu ba a san dalilan wadannan mutane masu dauke makamai ba, ana daukar zaman nasu a matsayin barazana ga tsaron rayuka da dukiyoyi al’ummar yankin.

A cewar wasikar, mazauna masarautar Rano mutane ne masu zaman lafiya da kullum suna gudanar da harkokinsu ba tare da haifar da tarzoma ba.

Ta ce a tsawon shekaru masarautar Rano ta samu zaman lafiya ba tare da wata matsala ba kuma hukumomin tsaro na iya shaida wannan tarihin da masarautar ke da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara