DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fãdar shugaban ƙasa na kitsa yadda za’a kama Peter Obi – Ofishin yãɗa labaran Obi

-

Ofishin yãda labarai na ɗan takaran shugaban ƙasa a jam’iyar Leba party a zaɓen shekara ta 2022 Peter yana zargin fadar shugaban ƙasa da kulla wa Peter Obi maƙarƙashiya da zummar ɓãta masa suna.

Ofishin na harkokin yada labaran Peter Obi ya musanta kalaman kakakin shugaba Tinubu Bayo Onanuga na alakanta ɗan takaran nasu da zanga-zangar da ake ƙoƙarin aiwatarwa a Najeriya.

Google search engine

Ofishin ya ce Bayo Onanuga ya wallafa a shafin sa na twitter cewa Obi da magoya bayan sa ya kamata a ɗora wa alhakin duk wani mummunan abu da zai auku a zanga-zanga da ake ƙoƙarin yi.

Saidai a sanarwar da ofishin na kula da harkar yaɗa labarai na Peter Obi ya fitar ta bakin Yunusa Tanko Asabat ɗinnan ya baiyana cewa zarge zarge marasa tushe da mai magana da yawun shugaban ya ke yi, ba komai bane illa munaƙisar yadda za’a samu dalilin kama Peter Obi a tauye masa hakki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara