DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za’a fara shari’ar mutanen da aka kama lokacin zanga-zanga a Abuja

-

A yau ne za a fara shari’ar masu zanga-zangar tsadar rayuwa a Abuja, Kano, Kaduna da Borno, kamar yadda mataimakin babban sufeton ‘yan sanda Dasuki Galadanchi ya bayyana.

Google search engine

Galadanchi ya bayyana hakan ne a wajen taron shekara-shekara na kungiyar lauyoyin Najeriya da aka kammala a Abuja.

Ya ce wadanda za a gurfanar gaban kotun su 126 ne da aka zargin su da laifin daga tutar kasar Rasha tare da neman a sauya tsarin mulki a lokacin zanga-zangar, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutane tare da sace dukiyoyin jama’a da na gwamnati a wasu jihohin kasar.

Lauyan mai kare hakkin bil’adama Femi Falana ne zai jagoranci sauran lauyoyin da za su kare masu zanga-zangar a gaban mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Lamido kan rawar Tinubu a soke zaɓen June 12

Fadar shugaban ƙasa ta musanta zargin tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, da cewa Tinubu ya goyi bayan soke zaɓen 12 ga watan Yuni, na 1993. A...

JAMB ta saka ranar da daliban da suka fuskanci matsaloli a UTME ta bana za su sake jarrabawar.

Hukumar JAMB ta bayyana Asabar, 28 ga watan Yunin, 2025 a matsayin ranar da za a gudanar da jarrabawar mop-up ta UTME na bana. A wata...

Mafi Shahara