HomeUncategorizedHisbah a Kano na tsare da kwamishina daga jihar Jigawa bisa zarginsa...

Hisbah a Kano na tsare da kwamishina daga jihar Jigawa bisa zarginsa da lalata da matar aure

-

Jami’an hukumar Hisbah a jihar Kano sun kama kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa Awwal Danladi Sankara bisa zargin lalata da matar aure.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa jami’an na Hisbah sun kama wanda ake zargin bayan da suka samu korafi daga mijin matar, da ya ce yana zargin akwai kullalliya tsakanin kwamishinan da matarsa.
Bayanai sun ce har yanzu ana tsare da wannan kwamishina a hukumar Hisbah ta Kano.
Mijin matar, ya ce suna da ‘ya’ya biyu da su ma ya diga ayar tambaya a kansu.
Hukumar Hisbah ta ce ta kama wanda ake zargin ne da misalin karfe 10 na daren Alhamis tare da matar a lokacin da suke kokarin shiga wani kango mallakin kwamishinan.
Hisbah ta ce a lokacin da aka isa da su hedikwatarta, wanda ake zargin ya amsa cewa ya taba kwanciya da matar sau uku kacal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img