DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin mutane a Jibia jihar Katsina

-

‘Yan ta’adda sun kai hari a Umguwar Bachaka cikin garin Jibia na jihar Katsina, inda suka kashe mutane 3 suka kuma sace da dama.
Wata majiya daga garin na Jibia da ta nemi kada a ambaci sunanta ta shaida wa DCL Hausa cewa maharan sun shiga garin ne da misalin karfe 11 na daren Asabar, suka fara harbin kan mai uwa da wabi da hakan ya jefa al’ummar yankin cikin razani.
Majiyar ta ce barayi sun rika bi gida-gida a cikin unguwar, inda suka ji wa karin wasu raunuka mafi yawansu kananan yara.
Har zuwa safiyar Lahadin nan dai, majiyar ta ce ba a iya tantance yawan mutanen da barayin dajin suka sace ba a Umguwar ta Bachaka da ke tsakiyar garin na Jibia.
Hukumomi a jihar Katsina ba su ce uffan ba game da batun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara