DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin mutane a Jibia jihar Katsina

-

‘Yan ta’adda sun kai hari a Umguwar Bachaka cikin garin Jibia na jihar Katsina, inda suka kashe mutane 3 suka kuma sace da dama.
Wata majiya daga garin na Jibia da ta nemi kada a ambaci sunanta ta shaida wa DCL Hausa cewa maharan sun shiga garin ne da misalin karfe 11 na daren Asabar, suka fara harbin kan mai uwa da wabi da hakan ya jefa al’ummar yankin cikin razani.
Majiyar ta ce barayi sun rika bi gida-gida a cikin unguwar, inda suka ji wa karin wasu raunuka mafi yawansu kananan yara.
Har zuwa safiyar Lahadin nan dai, majiyar ta ce ba a iya tantance yawan mutanen da barayin dajin suka sace ba a Umguwar ta Bachaka da ke tsakiyar garin na Jibia.
Hukumomi a jihar Katsina ba su ce uffan ba game da batun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ganga Miliyan 30 zuwa 50 na man kasar Venezuela za a sayar domin amfanin Amurka – Donald Trump

Farashin danyen mai ya kara faduwa a ranar Laraba bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Venezuela za ta mika wa Amurka ganguna miliyan...

Nijeriya na biyan tallafin lantarki kusan tiriliyan 2 a duk shekara

Rahotannin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) sun nuna cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe naira tiriliyan 1.98 a matsayin tallafin wutar lantarki cikin...

Mafi Shahara