DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun yi ajalin mutane a Jibia jihar Katsina

-

‘Yan ta’adda sun kai hari a Umguwar Bachaka cikin garin Jibia na jihar Katsina, inda suka kashe mutane 3 suka kuma sace da dama.
Wata majiya daga garin na Jibia da ta nemi kada a ambaci sunanta ta shaida wa DCL Hausa cewa maharan sun shiga garin ne da misalin karfe 11 na daren Asabar, suka fara harbin kan mai uwa da wabi da hakan ya jefa al’ummar yankin cikin razani.
Majiyar ta ce barayi sun rika bi gida-gida a cikin unguwar, inda suka ji wa karin wasu raunuka mafi yawansu kananan yara.
Har zuwa safiyar Lahadin nan dai, majiyar ta ce ba a iya tantance yawan mutanen da barayin dajin suka sace ba a Umguwar ta Bachaka da ke tsakiyar garin na Jibia.
Hukumomi a jihar Katsina ba su ce uffan ba game da batun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ka fito ka bayyana wa ‘yan Nijeriya hakikanin dalilin da ya sa ka canza hafsoshin tsaro – Bukatar ADC ga shugaba Tinubu

Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana gaskiya ga ’yan Nijeriya kan ainihin dalilan da suka sa aka yi gaggawar sauya shugabannin...

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya nada yayansa a matsayin Sarkin Duguri

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya naɗa yayansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sarkin sabon masarautar Duguri da aka ƙirƙira a jihar. Sakataren gwamnatin Jiha, Aminu...

Mafi Shahara