DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba ya daina amsa kiran Kwankwaso ta waya in ji jaridar Daily Nigerian

-

Rikicin jam’iyyar NNPP a jihar Kano ya sake daukar wani sabon salo bayan da Gwamna Abba Yusuf ya yi fatali da wasu tarurruka da kuma kin amsa kiran ubangidansa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Google search engine

A cewar jaridar Daily Nigerian wannan dai ya samo asali ne tun bayan bullen wata kungiya mai suna Abba Tsaya da Kafarka yayin da kiraye-kiraye daga ciki da wajen jam’iyyar ke kara ta’azzara na neman gwamnan ya samu ‘yancin kai daga ubangidan nasa.

Haka kuma an zargi sakataren gwamnatin jihar, Baffa Bichi da kwamishinan sufuri na jihar, Mohammed Diggol da kwamishinan ilimi Umar Doguwa da Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, sanata Kawu Sumaila, da dan majalisa, Ali Madaki da wasu ‘yan majalisar dokokin jihar Kano.

Wannan dai na zuwa ne bayan da a ranar 1 ga watan Nuwamba, wata babbar kotun jihar Abia ta ba da umarnin mayar da ikon jam’iyyar ga tsohon shugaban ta Boniface Aniebonam.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara