DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata budurwa ta hadu da ajalinta a kauyen jihar Katsina

-

Wasu mutane da har ya zuwa hada wannan rahoton, ba a san ko su wanene ba, sun yi wa wata budurwa mai suna Maryam Salisu Dangabas sanadin mutuwa a garin ‘Yanduna na karamar hukumar Baure jihar Katsina.

Bayanan da DCL Hausa ta samu daga makusantan budurwar mai kimanin shekaru 17 na nuna cewa ana zargin miyagun kafin su yi wannan aika-aika sai da suka kawar mata da budurcinta.

DCL Hausa ta tuntubi rundunar ‘yan sandan jihar ta Katsina inda kakakin rundunar Aliyu Abubakar Sadiq ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rundunar ‘yan sandan na ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Google search engine

Tuni aka yi jana’izar marigayiya Maryam Salisu kamar yadda addinin musulunci ya tanada a garin na ‘Yanduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara