DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata budurwa ta hadu da ajalinta a kauyen jihar Katsina

-

Wasu mutane da har ya zuwa hada wannan rahoton, ba a san ko su wanene ba, sun yi wa wata budurwa mai suna Maryam Salisu Dangabas sanadin mutuwa a garin ‘Yanduna na karamar hukumar Baure jihar Katsina.

Bayanan da DCL Hausa ta samu daga makusantan budurwar mai kimanin shekaru 17 na nuna cewa ana zargin miyagun kafin su yi wannan aika-aika sai da suka kawar mata da budurcinta.

DCL Hausa ta tuntubi rundunar ‘yan sandan jihar ta Katsina inda kakakin rundunar Aliyu Abubakar Sadiq ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rundunar ‘yan sandan na ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Google search engine

Tuni aka yi jana’izar marigayiya Maryam Salisu kamar yadda addinin musulunci ya tanada a garin na ‘Yanduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara