DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hedikwatar tsaron Nijeriya na neman karin wasu ‘yan ta’adda ruwa jallo

-

Mutanen da ake nema ruwa a jallo sun hada da Abu Khadijah, Abdurrahman, Dadi Gumba, Abu Muhammed, Usman Kanin Shehu, Abu Yusuf, Musa Wa’a, Ibrahim Suyeka, BA Sulhu da Idris Taklakse.

Google search engine

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban hafsan sojin kasar ya tabbatar da bullar wata sabuwar kungiyar ta’addanci da aka fi sani da ‘Lukarawas,’ wanda ke kara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin arewa maso yammacin Nijeriya.

Daraktan yada labaran hedikwatar tsaro, Maj Janar Edward Buba, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar a ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce sabuwar kungiyar ta’addancin ta bulla ne daga Jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da ya kai ga rugujewar hadin gwiwar sojoji tsakanin Nijeriya da Nijar din.

Ya kara da cewa ‘yan ta’addan sun fara kutsawa cikin yankunan arewacin jihohin Sokoto da Kebbi daga jamhuriyar Nijar da Mali, musamman bayan juyin mulkin da aka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnati na daf da fallasa masu ingiza ta’addanci a Nijeriya – Daniel Bwala

Hadimin shugaba Tinubu na Nijeriya Daniel Bwala ya bayyana cewa gwamnati na daf da kwarmata sunayen masu daukar nauyin ta'addanci a kasar. Bwala ya bayyana haka...

Ina fatan shugaba Tinubu ba zai sake tsayawa takara a 2027 ba – Hakeem Baba Ahmad

Tsohon mai bai wa shugaba Tinubu shawara kan harkokin siyasa Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya ce yana fatan shugaban Nijeriya ba zai sake neman kujerar shugabancin...

Mafi Shahara