DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hedikwatar tsaron Nijeriya na neman karin wasu ‘yan ta’adda ruwa jallo

-

Mutanen da ake nema ruwa a jallo sun hada da Abu Khadijah, Abdurrahman, Dadi Gumba, Abu Muhammed, Usman Kanin Shehu, Abu Yusuf, Musa Wa’a, Ibrahim Suyeka, BA Sulhu da Idris Taklakse.

Google search engine

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban hafsan sojin kasar ya tabbatar da bullar wata sabuwar kungiyar ta’addanci da aka fi sani da ‘Lukarawas,’ wanda ke kara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin arewa maso yammacin Nijeriya.

Daraktan yada labaran hedikwatar tsaro, Maj Janar Edward Buba, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar a ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce sabuwar kungiyar ta’addancin ta bulla ne daga Jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da ya kai ga rugujewar hadin gwiwar sojoji tsakanin Nijeriya da Nijar din.

Ya kara da cewa ‘yan ta’addan sun fara kutsawa cikin yankunan arewacin jihohin Sokoto da Kebbi daga jamhuriyar Nijar da Mali, musamman bayan juyin mulkin da aka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara