HomeUncategorizedHedikwatar tsaron Nijeriya na neman karin wasu 'yan ta'adda ruwa jallo

Hedikwatar tsaron Nijeriya na neman karin wasu ‘yan ta’adda ruwa jallo

-

Mutanen da ake nema ruwa a jallo sun hada da Abu Khadijah, Abdurrahman, Dadi Gumba, Abu Muhammed, Usman Kanin Shehu, Abu Yusuf, Musa Wa’a, Ibrahim Suyeka, BA Sulhu da Idris Taklakse.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban hafsan sojin kasar ya tabbatar da bullar wata sabuwar kungiyar ta’addanci da aka fi sani da ‘Lukarawas,’ wanda ke kara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin arewa maso yammacin Nijeriya.

Daraktan yada labaran hedikwatar tsaro, Maj Janar Edward Buba, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar a ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce sabuwar kungiyar ta’addancin ta bulla ne daga Jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da ya kai ga rugujewar hadin gwiwar sojoji tsakanin Nijeriya da Nijar din.

Ya kara da cewa ‘yan ta’addan sun fara kutsawa cikin yankunan arewacin jihohin Sokoto da Kebbi daga jamhuriyar Nijar da Mali, musamman bayan juyin mulkin da aka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img