DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar manyan likitoci tare da likitocin hakora na Nijeriya sun tsunduma yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai daga ranar Litinin dinnan

-

Likitoci

Lamarin da ake fargabar zai iya janyo tsayawar aiki a  kusan cibiyoyin kiwon lafiya 83, da kuma makarantun kiwon lafiya 64 a fadin kasar, kamar yadda shugaban kungiyar na kasa Farfesa Muhammad Muhammad wanda ya bayyana a wata tattaunawa ta musamman da jaridar Punch. 

Google search engine

A cikin wata sanarwar da kungiyar ta fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, ta ayyana cewa za ta shiga yajin aikin gargadi ne saboda gazawar gwamnatin tarayya wajen biyan bukatun kungiyar.

Yajin aikin ya soma a dukkan jami’o’i da manyan asibitocin Nijeriya daga Litinin 17 ga wata, zuwa Lahadi 24 ga watan Nuwamba, 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara