DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar manyan likitoci tare da likitocin hakora na Nijeriya sun tsunduma yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai daga ranar Litinin dinnan

-

Likitoci

Lamarin da ake fargabar zai iya janyo tsayawar aiki a  kusan cibiyoyin kiwon lafiya 83, da kuma makarantun kiwon lafiya 64 a fadin kasar, kamar yadda shugaban kungiyar na kasa Farfesa Muhammad Muhammad wanda ya bayyana a wata tattaunawa ta musamman da jaridar Punch. 

A cikin wata sanarwar da kungiyar ta fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, ta ayyana cewa za ta shiga yajin aikin gargadi ne saboda gazawar gwamnatin tarayya wajen biyan bukatun kungiyar.

Yajin aikin ya soma a dukkan jami’o’i da manyan asibitocin Nijeriya daga Litinin 17 ga wata, zuwa Lahadi 24 ga watan Nuwamba, 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato...

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Mafi Shahara