DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 6,tare da halaka wani manomi a Taraba

-

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas

Google search engine

‘Yan bindigar dai sun halaka manomin mai suna Alhaji Mai Wanda Maibultu a gonar sa a karshen makon da ya gabata,wanda yana daya daga cikin manyan manoma a kauyen.

Daily Trust ta rawaito cewa sauran manoma shidan da aka yi garkuwa da su,suna kauyen Garbatau, da ke tsakanin tsaunuka biyu a yanki.

Wani mazaunin garin Maihula, Adamu Dauda, ​​ya shaida wa Daily Trust cewa masu garkuwa da mutanen sun nemi iyalan manoman da suka sace, inda suka nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa.

Ya ce, ko a shekarar da ta gabata daruruwan masu garkuwa da mutane sun addabi yankin tare da yin garkuwa da manoma da dama, inda suka hana su girbin amfanin gonakinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotu za ta yanke hukunci kan belin Abubakar Malami a ranar 7 ga Janairu

Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta sanya 7 ga Janairu domin yanke hukunci kan bukatar beli da Abubakar Malami, tsohon Antoni-Janar na Tarayya...

EFCC ta yi watsi da zargin Gwamna Bala Mohammed na tsangwamar jami’an gwamnatinsa

Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa tu'annati a Nijeriya ta yi watsi da ikirarin da Bala Mohammed, Gwamnan Jihar Bauchi, ya yi...

Mafi Shahara