DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 6,tare da halaka wani manomi a Taraba

-

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas

Google search engine

‘Yan bindigar dai sun halaka manomin mai suna Alhaji Mai Wanda Maibultu a gonar sa a karshen makon da ya gabata,wanda yana daya daga cikin manyan manoma a kauyen.

Daily Trust ta rawaito cewa sauran manoma shidan da aka yi garkuwa da su,suna kauyen Garbatau, da ke tsakanin tsaunuka biyu a yanki.

Wani mazaunin garin Maihula, Adamu Dauda, ​​ya shaida wa Daily Trust cewa masu garkuwa da mutanen sun nemi iyalan manoman da suka sace, inda suka nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa.

Ya ce, ko a shekarar da ta gabata daruruwan masu garkuwa da mutane sun addabi yankin tare da yin garkuwa da manoma da dama, inda suka hana su girbin amfanin gonakinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin...

Mafi Shahara