DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 6,tare da halaka wani manomi a Taraba

-

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas

Google search engine

‘Yan bindigar dai sun halaka manomin mai suna Alhaji Mai Wanda Maibultu a gonar sa a karshen makon da ya gabata,wanda yana daya daga cikin manyan manoma a kauyen.

Daily Trust ta rawaito cewa sauran manoma shidan da aka yi garkuwa da su,suna kauyen Garbatau, da ke tsakanin tsaunuka biyu a yanki.

Wani mazaunin garin Maihula, Adamu Dauda, ​​ya shaida wa Daily Trust cewa masu garkuwa da mutanen sun nemi iyalan manoman da suka sace, inda suka nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansa.

Ya ce, ko a shekarar da ta gabata daruruwan masu garkuwa da mutane sun addabi yankin tare da yin garkuwa da manoma da dama, inda suka hana su girbin amfanin gonakinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan jihar Zamfara ya gabatar da kasafin kudi N861bn na 2026 ga majalisar dokokin jihar

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da kasafin kuÉ—i na Naira biliyan 861 na shekarar 2026 a gaban majalisar dokokin Jihar a Gusau, yana...

Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau domin tantancewa a matsayin jaakada

Shugaba Bola Tinubu ya ya aike da tsohon ministan cikin gida, Abdulrahman Dambazau, wanda ya taba zama shugaban sojin ƙasa, a matsayin jakada domin tantancewa...

Mafi Shahara