DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matawalle ya isa birnin Riyadh na Saudiyya wajen babban taron tsaro na kungiyar IMCTC

-

 

Google search engine


Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya Bello Matawalle ya isa birnin Riyadh na Saudiyya inda zai gana da Yariman kasar Mohammed bin Salman, a wani bangare na halatar taron kungiyar kasashen Musulmai da ke yaki da ‘yan ta’adda , IMCTC.

A yayin ziyarar aikin ministan ke yi a Saudiyya ya ziyarci hedikwatar kawancen kasashen Musulmi domin yaki da ta’addanci, inda ya yi godiya ga Sakatare Janar na kungiyar ta IMCTC, bisa gudunmuwar da suke bai wa Nijeriya ta hanyar horas da sojojinta dubarun yaki da ta’addanci.






LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara