DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta kama wani dan kasar Aljeriya mai shekaru 58 bisa zargin sa da safarar makamai ta kan iyaka

-

‘Yan sanda

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Dalijan ne ya bayyana haka a Gusau ranar Talata.

Google search engine

Ya ce ‘yan sandan sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda 16, a atisaye daban-daban a cikin makonni uku da suka gabata.

Ya kara da cewa sun kuma samu nasarar kwato bindiga kirar Pistol da aka kera a cikin gida daga hannun wani da ake zargi da ke kera makamai da ke Jos, Filato.

A cewar sa bisa bayanan sirri da suka samu sun gano tare da kama wani mai kera makamai a Jos, kuma sun bi sawun wani da ake zargi da safarar makamai daga Aljeriya a kan iyakar Illela inda suka samu nasarar kama shi.

Wanda ake zargin dan kasar Algeria, ya shaidawa ‘yan sanda cewa ya shafe shekaru takwas yana aikata wannan laifin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja, Kano da Rivers

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a, jami’an tsaro da jami’an Hukumar zaɓe Mai zaman kanta (INEC) da su gudanar...

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji "Armed Forces College of Medicine and Health Sciences" a matsayin wani mataki na...

Mafi Shahara