DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta kama wani dan kasar Aljeriya mai shekaru 58 bisa zargin sa da safarar makamai ta kan iyaka

-

‘Yan sanda

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Dalijan ne ya bayyana haka a Gusau ranar Talata.

Google search engine

Ya ce ‘yan sandan sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda 16, a atisaye daban-daban a cikin makonni uku da suka gabata.

Ya kara da cewa sun kuma samu nasarar kwato bindiga kirar Pistol da aka kera a cikin gida daga hannun wani da ake zargi da ke kera makamai da ke Jos, Filato.

A cewar sa bisa bayanan sirri da suka samu sun gano tare da kama wani mai kera makamai a Jos, kuma sun bi sawun wani da ake zargi da safarar makamai daga Aljeriya a kan iyakar Illela inda suka samu nasarar kama shi.

Wanda ake zargin dan kasar Algeria, ya shaidawa ‘yan sanda cewa ya shafe shekaru takwas yana aikata wannan laifin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara