DCL Hausa Radio
Kaitsaye

WAEC, ta haramta wa wasu makarantu 13 a jihar Kogi yin jarrabawar, bisa zargin su da satar jarrabawa a shekarar 2023/2024

-

 

WAEC

Google search engine

Kwamishinan Ilimi na jihar, Wemi Jones ne ya bayyana hakan a lokacin wani taro da suka yi da wasu shugabanni da masu kula da WAEC.

Ya ce gwamnati ta sha alwashin hukunta shugabannin makarantu da malaman da suke kula da dalibai suka taimaka wajen lalata harkar jarrabawa a jihar.

Jones ya jaddada cewa aikata hakan babban laifine kuma gwamnati za ta hukunta duk wanda ta kama yana da hannu a ciki,daga yanzu za a gurfanar da duk wanda aka kama da aikata laifin satar jarabawa kuma a gurfanar da shi gaban kotu kamar yadda dokar ilimi ta jihar Kogi ta tanada.

Ya bayyana cewa za a kafa wani kwamiti wanda babban sakatare na ma’aikatar ilimi zai jagoranta domin bincikar mutanen da WAEC ta ke tuhumar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara