DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya rushe majalisar gudanarwa ta jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke jihar Anambra

-

Shugaba Tinubu

A cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasar shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar ya ce rushe majalisar gudanarwar ya biyo bayan rahotannin da ke nuna cewa akwai wasu abubuwa da majalisar ke yi ba bisa ka’ida ba.

Google search engine

Gwamnatin ta nuna damuwarta kan yadda majalisar ta nuna rashin kula da dokokin jami’ar wajen zaben wasu shugabanni.

Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya kuma rushe shugabancin Engr. Ohieku Muhammed Salami a matsayin Pro-chancellor kuma shugaban majalisar gudanarwa na jami’ar tarayya ta kimiyar lafiya dake Otukpo a jihar Benue.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara