Gwamna Zulum na jihar Borno ya kaddamar da raba tallafin tireloli 100 na abinci daga Shugaba Tinubu

-

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya fara rabon tireloli 100 na kayan abinci da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba wa mazauna Jihar Borno. An fara rabon kayan abincin, wanda ya kunshi masara, gero, da dawa, ga gidajen da suka fi bukata a Gamboru, Ngala, da wasu al’ummomi da aka kebe saboda mamakon ruwa da ambaliyar da suka shafe watanni hudu.
Da yake magana yayin kaddamar da rabon kayan, Gwamna Zulum ya jaddada muhimmancin tallafin wajen rage wahalhalun da al’ummar suka fuskanta, sannan ya gode wa Shugaba Tinubu da hukumomin tarayya da suka bada gudummawa. Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bayar da karin tireloli 100 na shinkafa domin tallafa wa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri.
Zulum ya bayyana cewa gwamnatinsa tana ci gaba da sauya matsaya daga rabon kayan abinci zuwa samar da hanyoyin dogaro da kai, ciki har da kafa tsarin ban ruwa domin noma na tsawon shekara a cikin al’ummomin da aka sake tsugunar da su, musamman a Ngala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara