DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar “Independent Hajj Reporters” ta bukaci NAHCON ta kafa kwamitin da zai sanya ido kan yadda za’a mayarwa mahajjata kudadensu

-

Kungiyar nan mai sanya ido kan harkokin aikin hajji a Nijeriya “Independent Hajj Reporters” ta yi kira ga hukumar alhazzai ta kasa NAHCON da ta kafa wani kwamiti na musamman da zai san ya ido akan aikin mayarwa mahajjata 95,000 da suka yi aikin hajji a shekara ta 2023 kudaden su.
 
A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Ibrahim Muhammad, ya ce wannan ya zama tilas domin magance duk wasu korafe-korafe da ke biyowa bayan an mayar da kudade.
  
A saboda haka shugaban kungiyar Ibrahim Muhammad ya bukaci NAHCON ta fitar da bayanan kudin da ta tura, kuma ta tilastawa hukumomin bayyana yawan mutanen da za a mayarwa kudaden tare da kafa wani kwamiti da zai kunshi har da ‘yan jarida da zai tabbatar da cewa an biya mahajjatan hakkokinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara