DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar “Independent Hajj Reporters” ta bukaci NAHCON ta kafa kwamitin da zai sanya ido kan yadda za’a mayarwa mahajjata kudadensu

-

Kungiyar nan mai sanya ido kan harkokin aikin hajji a Nijeriya “Independent Hajj Reporters” ta yi kira ga hukumar alhazzai ta kasa NAHCON da ta kafa wani kwamiti na musamman da zai san ya ido akan aikin mayarwa mahajjata 95,000 da suka yi aikin hajji a shekara ta 2023 kudaden su.
 
A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Ibrahim Muhammad, ya ce wannan ya zama tilas domin magance duk wasu korafe-korafe da ke biyowa bayan an mayar da kudade.
  
A saboda haka shugaban kungiyar Ibrahim Muhammad ya bukaci NAHCON ta fitar da bayanan kudin da ta tura, kuma ta tilastawa hukumomin bayyana yawan mutanen da za a mayarwa kudaden tare da kafa wani kwamiti da zai kunshi har da ‘yan jarida da zai tabbatar da cewa an biya mahajjatan hakkokinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara