DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aunin tattalin arziki GDP na Nijeriya ya karu da kashi 3.46 – hukumar kididdiga NBS

-

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ta ce ma’aunin tattalin arzikin Nijeriya ya karu zuwa kashi 3.46 a rubu’i na uku na shekarar 2024, inda ya kai naira tiriliyan 71.1.
Wani bayani da Shugaban hukumar kididdiga ta kasa Prince Adeyemi Adeniran Adedeji, ya ce an samu ci gaba da kashi 0.92 idan aka kwatanta da rubu’i na uku na shekara ta 2023 da ma’aunin GDP ya kai kashi 2.54.
Bayanin ya kara da cewa ma’aunin a rubu’i na uku ya yi sama da kashi 0.27 idan aka kwatanta da rubu’i na biyu na wannan shekara ta 2024.
Wannan ci gaban da aka samu, hukumar kididdiga NBS ta alakanta shi da ci gaban da aka samu fannin noma da kasuwanci da sadarwa da kuma harkar gidaje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotu ta daure wani dan Nijeriya a Amurka kan laifin zambar kudin gado

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai suna Ehis Lawrence Akhimie hukuncin daurin shekaru fiye da takwas bayan an same shi...

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Mafi Shahara