DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta samu nasarar janyo dala biliyan 1.27 daga masu saka hannun jari na Kasashe mambobin BRICS

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Nijeriya ta samu nasarar janyo masu zuba hannun jari daga kasashen BRICS wadanda suka zuba jarin dala biliyan 1.27 a watan Yunin 2024 wanda yasa hannun jarin kasashen waje ya karu daga dala miliyan 438.72 da aka samu a shekarar 2023.
Kungiyar kasashen BRICS da tattalin arzikinsu ke bunkasa wacce kuma ke neman zama kishiya ga kasashen Yamma sun hada da Brazil, Russia, India, China, South Africa, da kuma Iran, 
Akwai kuma kashe irin su Egypt, Ethiopia, da ma Hadaddiyar Daular Larabawa dukkanin su cikin ƙungiyar ta BRICS
Da yake jawabi a wurin taron dandalin bankunan nahiyar Afirka da ƙasar China, Kashim Shettima wanda ya samu wakilcin mai baiwa shugaban kasa shawara kan ayyuka Dr Aliyu Modibbo, ya ce alaƙar Nijeriya da Kasashen BRICS na kara karfi musamman wajen bunkasa tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sojoji sun ceto wani mutum da shanu a tsakanin Kano da Katsina

Sojojin rundunar haɗin gwiwa na Joint Task Force sun yi nasarar ceto wani mutum da aka sace tare da kwato wasu shanu da ‘yan bindiga...

Majalisar Dokokin Taraba ta musanta cewa Kakakinta ya raba Naira 1000 a matsayin barka da Kirsimeti

Majalisar Dokokin Jihar Taraba tare da Zing Watch Group sun musanta rahotannin da ke yawo cewa Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Taraba, John Bonzena, ya raba...

Mafi Shahara