DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta samu nasarar janyo dala biliyan 1.27 daga masu saka hannun jari na Kasashe mambobin BRICS

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Nijeriya ta samu nasarar janyo masu zuba hannun jari daga kasashen BRICS wadanda suka zuba jarin dala biliyan 1.27 a watan Yunin 2024 wanda yasa hannun jarin kasashen waje ya karu daga dala miliyan 438.72 da aka samu a shekarar 2023.
Kungiyar kasashen BRICS da tattalin arzikinsu ke bunkasa wacce kuma ke neman zama kishiya ga kasashen Yamma sun hada da Brazil, Russia, India, China, South Africa, da kuma Iran, 
Akwai kuma kashe irin su Egypt, Ethiopia, da ma Hadaddiyar Daular Larabawa dukkanin su cikin ƙungiyar ta BRICS
Da yake jawabi a wurin taron dandalin bankunan nahiyar Afirka da ƙasar China, Kashim Shettima wanda ya samu wakilcin mai baiwa shugaban kasa shawara kan ayyuka Dr Aliyu Modibbo, ya ce alaƙar Nijeriya da Kasashen BRICS na kara karfi musamman wajen bunkasa tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato...

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Mafi Shahara