DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta samu nasarar janyo dala biliyan 1.27 daga masu saka hannun jari na Kasashe mambobin BRICS

-

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa Nijeriya ta samu nasarar janyo masu zuba hannun jari daga kasashen BRICS wadanda suka zuba jarin dala biliyan 1.27 a watan Yunin 2024 wanda yasa hannun jarin kasashen waje ya karu daga dala miliyan 438.72 da aka samu a shekarar 2023.
Kungiyar kasashen BRICS da tattalin arzikinsu ke bunkasa wacce kuma ke neman zama kishiya ga kasashen Yamma sun hada da Brazil, Russia, India, China, South Africa, da kuma Iran, 
Akwai kuma kashe irin su Egypt, Ethiopia, da ma Hadaddiyar Daular Larabawa dukkanin su cikin ƙungiyar ta BRICS
Da yake jawabi a wurin taron dandalin bankunan nahiyar Afirka da ƙasar China, Kashim Shettima wanda ya samu wakilcin mai baiwa shugaban kasa shawara kan ayyuka Dr Aliyu Modibbo, ya ce alaƙar Nijeriya da Kasashen BRICS na kara karfi musamman wajen bunkasa tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara