DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta ki amincewa hukumar EFCC ta gurfanar da Yahaya Bello ba tare da lauyansa ba

-

Kotun tarayya dake Abuja ta dage sauraren karar da hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta shigar akan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello har sai ranar 13 ga watan Disamba 2024.
Mai Shari’a Emeka Nwite ta dage zaman ne bayan da a farko ta dage sauraren karar har sai 21 ga watan Janairu 2025.
Sai dai lokacin da aka tambayi Yahaya Bello lauyansa, ya shaidawa an sanar da shi zaman kotun ne cikin dare hakan ya sa bai samu damar kiran lauyoyinsa ba.
Sai dai alkalin kotu ya umurci EFCC ta ci gaba da tsare shi kuma ta sanar da lauyoyinsa ranar 13 ga watan Disamba da kotun za ta sake zama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Mafi Shahara