DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta ki amincewa hukumar EFCC ta gurfanar da Yahaya Bello ba tare da lauyansa ba

-

Kotun tarayya dake Abuja ta dage sauraren karar da hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta shigar akan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello har sai ranar 13 ga watan Disamba 2024.
Mai Shari’a Emeka Nwite ta dage zaman ne bayan da a farko ta dage sauraren karar har sai 21 ga watan Janairu 2025.
Sai dai lokacin da aka tambayi Yahaya Bello lauyansa, ya shaidawa an sanar da shi zaman kotun ne cikin dare hakan ya sa bai samu damar kiran lauyoyinsa ba.
Sai dai alkalin kotu ya umurci EFCC ta ci gaba da tsare shi kuma ta sanar da lauyoyinsa ranar 13 ga watan Disamba da kotun za ta sake zama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya sauke farashin litar man fetur zuwa N699

Kamfanin Dangote Refinery ya sake rage farashin Fetur daga N828 zuwa N699 a kowace lita, an samu ragin da ya kai N129 ko kusan kashi...

Tinubu ne ke da rijayen kuri’un Rivers a zaben 2027 – Gwamna Fubara

Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya bayyana cewa zai jagoranci kokarin tabbatar da nasarar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027, yana mai cewa hadin kai...

Mafi Shahara