DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu sana’ar ‘DJ’ sun yi zanga-zanga ga hukumar Hisbah a Katsina

-

Masu sana’ar DJ da ke nishadantar da taron mutane a lokuttan bukukuwa sun cika makil a filin taro na Kangiwa Square a jihar Katsina, inda suka yi zanga-zanga ga hukumar Hisbah ta jihar bisa dakatar da sana’ar su da ta yi na tsawon watanni 8.
Masu sana’ar sun ma roki gwamnatin jihar Katsina da ta sa baki a bar su, su ci gaba da gudanar da sana’ar su da suka ce ba su takura wa kowa kuma ba su shiga hakkin kowa. Sun kuma koka kan cewa hukumar Hisbah din ta kwace musu kayan aiki na milyoyin Nairori.
Zanga-zangar ta su, ta yi daidai da lokacin da Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ke bude aikin fadada titin Kofar Soro zuwa Kofar Guga cikin kwaryar birnin Katsina da aka kammala kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.
An dai ga matasan dauke kwalaye masu rubutun da ke nuna irin halin da suka ce suna ciki tun bayan dakatar musu da sana’ar da hukumar ta Hisbah ta yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara