DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wuta ta katse a Nijeriya bayan da kamfanonin sarrafa gas suka daina ba wa kamfanonin samar da lantarki

-

Wuta ta katse a Nijeriya bayan da kamfanonin sarrafa gas suka daina ba wa kamfanonin samar da lantarki

Wani bincike da jaridar PUNCH ta gudanar ya nuna cewa kamfanonin da ke samar da gas sun dakatar da bai wa kamfanonin samar da wutar lantarki iskar gas, sakamakon rashin biyan basussukan da aka tara musu tsawon lokaci. 

Google search engine

Babbar jami’ar kungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ce ta sanar da hakan a wata tattaunawa da jaridar PUNCH a ranar Laraba, inda ta jaddada cewa kamfanonin da ke samar da iskar gas sun sanar da daukacin kamfanoninsu a hukumance cewa sun dakatar da samar musu da iskar gas. 

An dai dakatar da samar da iskar gas din ne bayan da hukumar kula da harkokin man fetur ta Nijeriya ta umarci masu samar da iskar gas din da su daina ba wa kamfanonin samar da lantarki da ake bin su bashi.

Wannan lamarin dai shi ne ya haifar da katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya, wanda a halin yanzu, sama da kashi 70 cikin 100 na wutar lantarkin kasar ana samar wa ne ta hanyar iskar gas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An dage jana’izar marigayi Muhammad Buhari zuwa ranar Talata -Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da shirye-shiryen jana'izar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga Yuli,...

Jam’iyyar ADC ta sanar da kwana uku na alhinin rashin tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari

Jam’iyyar ADC ta bayyana kwanaki uku na zaman makoki ga mambobinta don girmama marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi...

Mafi Shahara