DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wuta ta katse a Nijeriya bayan da kamfanonin sarrafa gas suka daina ba wa kamfanonin samar da lantarki

-

Wuta ta katse a Nijeriya bayan da kamfanonin sarrafa gas suka daina ba wa kamfanonin samar da lantarki

Wani bincike da jaridar PUNCH ta gudanar ya nuna cewa kamfanonin da ke samar da gas sun dakatar da bai wa kamfanonin samar da wutar lantarki iskar gas, sakamakon rashin biyan basussukan da aka tara musu tsawon lokaci. 

Babbar jami’ar kungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ce ta sanar da hakan a wata tattaunawa da jaridar PUNCH a ranar Laraba, inda ta jaddada cewa kamfanonin da ke samar da iskar gas sun sanar da daukacin kamfanoninsu a hukumance cewa sun dakatar da samar musu da iskar gas. 

An dai dakatar da samar da iskar gas din ne bayan da hukumar kula da harkokin man fetur ta Nijeriya ta umarci masu samar da iskar gas din da su daina ba wa kamfanonin samar da lantarki da ake bin su bashi.

Wannan lamarin dai shi ne ya haifar da katsewar wutar lantarki a fadin Nijeriya, wanda a halin yanzu, sama da kashi 70 cikin 100 na wutar lantarkin kasar ana samar wa ne ta hanyar iskar gas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara