DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zargin da Janar Tiani ya yi kan alakar Nijeriya da Faransa babu kanshin gaskiya a ciki – Gwamnatin Tarayya

-

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da kakkausar murya, ta sa kafa ta shure zarge-zargen Shugaban mulkin soja na Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya yi ma cewa akwai wata boyayyiyar alaka tsakanin Nijeriya da kasar Faransa.
An dai ga faifan bidiyon Tiani na yawo a kafafen sada zumunta, inda ya ke zargin cewa akwai wata alaka da ake yi wa nuku-nuku tsakanin Nijeriya da Faransa.
A cikin wata sanarwa daga Ministan yada Labaran Nijeriya Mohamed Idris, da DCL Hausa ta samu kwafi, ta ce zancen-zuci ne kawai Janar Tiani ke sakawa, amma babu wata boyayyiyar alaka tsakanin kasashen biyu da ma kowace kasa da ke da barazana ga kasar Nijar.
Sanarwar ta ce a matsayin Shugaba na Tinubu na shugaban kungiyar ECOWAS ya nuna dattako da iya tafiyar da lamurra, har ma aka bar kofar sasanci na Nijar da sauran kasashe na su koma cikin kungiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara