HomeUncategorizedZargin da Janar Tiani ya yi kan alakar Nijeriya da Faransa babu...

Zargin da Janar Tiani ya yi kan alakar Nijeriya da Faransa babu kanshin gaskiya a ciki – Gwamnatin Tarayya

-

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da kakkausar murya, ta sa kafa ta shure zarge-zargen Shugaban mulkin soja na Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya yi ma cewa akwai wata boyayyiyar alaka tsakanin Nijeriya da kasar Faransa.
An dai ga faifan bidiyon Tiani na yawo a kafafen sada zumunta, inda ya ke zargin cewa akwai wata alaka da ake yi wa nuku-nuku tsakanin Nijeriya da Faransa.
A cikin wata sanarwa daga Ministan yada Labaran Nijeriya Mohamed Idris, da DCL Hausa ta samu kwafi, ta ce zancen-zuci ne kawai Janar Tiani ke sakawa, amma babu wata boyayyiyar alaka tsakanin kasashen biyu da ma kowace kasa da ke da barazana ga kasar Nijar.
Sanarwar ta ce a matsayin Shugaba na Tinubu na shugaban kungiyar ECOWAS ya nuna dattako da iya tafiyar da lamurra, har ma aka bar kofar sasanci na Nijar da sauran kasashe na su koma cikin kungiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img