Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya tabbatar wa ‘yan kasar kudirin gwamnatinsa na bunÆ™asa samar da abinci da kuma rage hauhawar farashi zuwa kashi 15 ta hanyar bunkasa tattalin arziki a sabuwar shekarar 2025
A cikin sakon barka da sabuwar shekara da ya aike wa ‘yan Nijeriya, Shugaba Tinubu ya bayyana saukar farashin fetur da Æ™aruwar kudaden ajiya na kasa da kuma farfaÉ—owar darajar naira, a matsayin wasu alamomin da ke nuna cewa tattalin arzikin kasar na kan hanyar ci gaba.
Shugaban ya kara da cewa kasuwar hannun jari ta kasar na kara bunkasa tare da samar da kudaden shiga haka kuma masu zuba hannun jari daga kasashen waje na ci gaba da ƙaruwa.