DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu kanshin gaskiya a zancen cewa Kwankwaso zai koma APC – Hashimu Dungurawa na NNPP a Kano

-

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso

 Shugaban jam’iyyar NNPP Hashim Sulaiman Dungurawa, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya sake duba ga manufofin gwamnatinsa da al’umma ba sa goyon baya, ko kuma ya fuskanci shan kaye a babban zabe mai zuwa.

Dungurawa ya kuma ce batun da ake cewa jagoran jam’iyyar Rabiu Musa Kwankwaso na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC ba gaskiya ba ne.

Google search engine

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Alhamis, Dungurawa ya jaddada cewa jam’iyyar NNPP na kara samun tagomashi tare da kara fadada a dukkan jihohin Nijeriya 36, wanda hakan zai basu damar samun kujerun gwamnonin wasu jihohi a zaben 2027.

Ya bukaci gwamnatin tarayya da ta mayar da hankali wajen aiwatar da manufofin da za su rage wa ‘yan Nijeriya radadin da suke ciki da kuma kauce wa bullo da tsare-tsaren da suka saba wa muradun jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara