DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsoma baki da manyan arewa ke yi wajen tsayar da ɗan takara ci baya ne ga dimukradiyya – Kwankwaso

-

Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zargi wasu mutane da yace na ayyana kan su a matsayin jagororin arewa da yin katsalandan a sha’anin zaben dan takarar shugabancin kasa.
A zantawarsa da BBC Hausa, jagoran darikar Kwankwasiyya, ya yi zargin cewa hakan na kawo ci baya ga dimukradiyyar kasar tare da raba kan al’umma har ta kai ga an zabi dan takarar da bai cancanta ba.
Kwankwaso kuma tsohon gwamnan Kano ya jaddada bukatar jagororin su dauki darasi daga abubuwan da suka faru a baya tare da tsame bakinsu a duk wani sha’ani na zaben dan takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara