DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An sako wasu mata ‘yan Nijeriya bayan shafe watanni 10 tsare a Saudiyya bisa zargin safarar kwayoyi

-

Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ta sanar da sakin wasu mata uku ‘yan Nijeriya da aka gurfanar a kasar Saudiyya bisa zargin safarar miyagun kwayoyi, bayan sun shafe watanni 10 a tsare gidan kaso.
Sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar Kimiebi Ebienfa ya fitar, ta tabbatar da sako matan bayan an bi hanyoyin diflomasiyya.
A watan Maris na 2024 ne aka damke Hadiza Abba, da Fatima Umate Malah, da kuma Fatima Kannai Gamboil a filin jirgin saman kasa da kasa na Yarima Mohammad bin Abdulaziz da ke birnin Madinah.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara