DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An sako wasu mata ‘yan Nijeriya bayan shafe watanni 10 tsare a Saudiyya bisa zargin safarar kwayoyi

-

Ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya ta sanar da sakin wasu mata uku ‘yan Nijeriya da aka gurfanar a kasar Saudiyya bisa zargin safarar miyagun kwayoyi, bayan sun shafe watanni 10 a tsare gidan kaso.
Sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar Kimiebi Ebienfa ya fitar, ta tabbatar da sako matan bayan an bi hanyoyin diflomasiyya.
A watan Maris na 2024 ne aka damke Hadiza Abba, da Fatima Umate Malah, da kuma Fatima Kannai Gamboil a filin jirgin saman kasa da kasa na Yarima Mohammad bin Abdulaziz da ke birnin Madinah.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara