DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sake nada kwamishinoni

-

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nadin wasu mukamai na wasu muhimman mutane a gwamnatinsa ciki har da Ahmad Muhammad Speaker a matsayin mashawarci kan yada labarai.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce sauran mukaman sun hada da Injiya Ahmad a matsayin mai baiwa gwamna shawara bangaren ayyuka da Malam Sani Abdullahi Tofa bangaren ayyuka na musamman.
Gwamnan ya kuma nada Malam Sani Tofa a matsayin Khadi na kotun shari’a, kazalika da da Honarabul Ibrahim Jibrin Fagge a matsayin shugaban hukumar kula da ma’aikatan kananan hukumomi da sai Hajia Ladidi Ibrahim Garko a matsayin shugabar hukumar kula da ma’aikatan jihar Kano.
Sanarwar ta ce, gwamnan zai rantsar da wadanda aka baiwa mukaman a gobe Litinin 6 ga watan Janairun a fadar gwamnatin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara