DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iyalan waɗanda harin jirgin sama ya rutsa da su a jihar Zamfara sun nemi a biya su diyya

-

Iyalan wadanda harin jirgin saman Sojin Najeriya ya yi ajalin su bisa kuskure a kananan hukumomi Zurmi da Maradun a jihar Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya.

Harin wanda jirgin ya kai na ranar 11 ga Janairu 2024 a kauyen Gidan Kara da Malikawa sai Sakida tare da Kakidawa da Tungar Labbo dake Gidan Goga a kananan hukumomin na Zurmi da Maradun, ya yi sanadiyyar rayukan mutum 15 da raunata 9.
Kawo yanzu wadan da suka samu rauni na cigaba da karbar kulawar likitoci a Asibitin Kaura -Namoda dake jihar.
Daya daga cikin iyalan wanda suka nemi biyan diyyar Muhammad Aminu, a zantawar sa Jaridar Daily Trust ta wayar Tarho , ya ce suna kira ga gwamnatin jihar Zamfara da ta Najeriya da su gaggauta biyan su diyya sakamakon halin da aka jefa su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara