DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iyalan waɗanda harin jirgin sama ya rutsa da su a jihar Zamfara sun nemi a biya su diyya

-

Iyalan wadanda harin jirgin saman Sojin Najeriya ya yi ajalin su bisa kuskure a kananan hukumomi Zurmi da Maradun a jihar Zamfara sun nemi gwamnati ta biya su diyya.

Harin wanda jirgin ya kai na ranar 11 ga Janairu 2024 a kauyen Gidan Kara da Malikawa sai Sakida tare da Kakidawa da Tungar Labbo dake Gidan Goga a kananan hukumomin na Zurmi da Maradun, ya yi sanadiyyar rayukan mutum 15 da raunata 9.
Kawo yanzu wadan da suka samu rauni na cigaba da karbar kulawar likitoci a Asibitin Kaura -Namoda dake jihar.
Daya daga cikin iyalan wanda suka nemi biyan diyyar Muhammad Aminu, a zantawar sa Jaridar Daily Trust ta wayar Tarho , ya ce suna kira ga gwamnatin jihar Zamfara da ta Najeriya da su gaggauta biyan su diyya sakamakon halin da aka jefa su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Farfesoshin Nijeriya na cikin jerin na nahiyar Afrika da ba su da albashi mai kyau

Bayanan da jaridar Punch ta tattaro sun ce malamin jami'a a Nijeriya da ya kai matakin farfesa na samun matsakaicin albashi na dala 366 (kimanin...

Mafi Shahara