DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Al-Hilal ba za ta yi wa Neymar Jnr rijista ba

-

Kungiyar kwallon kafa ta Al Hilal dake kasar Saudi Arabia, ba zata yi wa gwarzon dan wasan kasar Brazil Neymar Junior rijistar buga zagaye na biyu na gasar kakar wasannin firimiyar kasar ba ta 2025.

Hakan ya biyo bayan nazarin lafiyar dan wasan da tawagar ta yi na irin gudunmowar da zai bawa kungiyar.
A baya Neymar ya samu zunzurutun kudi Euro Miliyan 101 a shekarar 2024, a wasanni biyu kacal da ya shafe mintuna 42 a cikin filin wasa.
Ya shafe tsawon watanni 6, ya na fama da jinyar rauni abinda ya sa a yanzu haka Al Hilal ke dari -darin tsawaita kwantiragin sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara