DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya umarci da a mayar da wadan da suka jikkata sakamakon fashewar tankar mai a jihar Neja zuwa manyan cibiyoyin kiwon lafiya domin ci gaba da basu kulawa ta musamman

-

Shugaba Tinubu

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga ministan yada labarai Rabiu Ibrahim ya fitar a ranar Litinin ya ce an kwantar da marasa lafiyan guda 20 a asibitin kwararru na Gwagwalada da ke Abuja.Hakazalika an kai karin wasu mutum biyu zuwa cibiyar kiwon lafiya ta tarayya dake Jabi, Abuja.

Google search engine

Sanarwar ta kara da cewa dukkan marasa lafiyan suna tare da ma’aikatan jinya da ‘yan uwan su a wuraren da aka kaisu don basu kulawa ta musamman.

Lamarin fashewar tankar mai na ci gaba da yawaita a ‘yan shekarun nan, da ko a farkon watan Janairu, akalla mutane biyar ne suka rasu a lokacin da wata tankar mai dauke da man fetur ta kama da wuta a yankin Agbor na jihar Delta.

 A watan Oktoban shekarar da ta gabata ma wata tankar mai da ta fadi a jihar Jigawa ta kashe mutane sama da 170 tare da jikkata wasu da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara